1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rushewar gini a Kenya ya halaka dalibai

Lateefa Mustapha Ja'afar
September 23, 2019

Kimanin dalibai bakwai ne suka rasa rayukansu yayin da wasu 64 suka jikkata sakamakon rushewar ginin wata makaranta a Nairobi babban birnin kasar Kenya.

https://p.dw.com/p/3Q6uj
Kenia eingestürztes Schulgebäude in Nairobi
Yara sun halaka a wata makaranta a Kenya bayan da ginita ya rushe Hoto: DW/S. Wasilwa

Tuni dai hukumomin kasar da suka tabbatar da afkuwar wannan ibtila'i ta bakin  da kakakin fadar gwamnati Cyrus Oguna. Rahotanni sun nunar da cewa an dauki yaran da suka jikkata zuwa babban asibiti na Kenyatta National Hospital a kan babura, kasancewar jami'an agaji ba su iso wajen ba sai bayan sa'a guda da rabi. Dalibai biyu cikin wadanda ke kwance a asibitin dai na cikin mawuyacin hali.