1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kazamin fada a kasar Kongo

April 2, 2013

An yi wani artabu tsakanin sojojin Kongo da wasu mayakan kungiyar Mai-Mai da ke fafutukar kwato 'yancin yankin Katanga,inda mutane 23 suka mutu 54 suka samu raunuka

https://p.dw.com/p/187un
Hoto: Reuters

 A wani rikicin da ya barke a 'yan kwanakin baya bayan nan a kasar ta Jamhuriyar Demokradiyar Kongo, rahotani sun tabbatar da kimanin mutane 23 ne dai suka kwanta damarsu tun bayan barkewar rikicin a makon nan da ya shige a yankin Lubumbashi inji kakakin gwamnatin kasar ta Kongo.

A kwanan baya ne dai aka yi wani artabu tsakanin dakarun gwamnatin da mayakan kungiyar Mai-Mai  yayinda sama da mutane 54 suka samu raunuka ciki har da fararen hula kamar yadda sanarwar ta gwamnatin ta bayanar.

Rahotani sun ce mayakan sun kutso ne daga yankin katanga mai dimbin arzikin ma'adinai inda sukayi masayar wuta da dakarun gwamntai da suka samu goyon bayan sojojin kiyaye zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya.

Dama dai tun wajajan shekarun 1960 ne yankin na Katanga ya tada kayar baya na bukatar samun 'yancin gashin kansa a matsayin kasa mai cikakken iko.

Mawallafi: Issoufou Mamane

Edita : Saleh Umar Saleh