1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zabtarewar kasa ta kashe rayuka a Kamaru

Abdourahamane Hassane
October 30, 2019

An samu zabtarewar kasa a Bafoussam da ke a yammacin Kamaru wanda lamarin ya rutsa da rayukan jama'a da dama a sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya.

https://p.dw.com/p/3SAgD
Wannan wani tsohon hoto ne na zabtarewar kasa da muka yi amfani da shi
Wannan wani tsohon hoto ne na zabtarewar kasa a Afirka da muka yi amfani da shiHoto: picture-alliance/Photoshot

Akalla mutane guda 42 suka rasa rayukansu bayan da aka samu zabtarewar kasa a Bafoussam da ke a yammacin Kamaru, gidaje da dama lakar da ta malala ta binne a sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya a yankin. A cikin wani jawabin ta kafofin sadarwa na gwamnati, shugaba kasar Paul Biya ya yi ta'aziya zuwa ga iyalen wadanda suka yi rashin. A cikin watan Yuli na shekara bara ma an samu zabtarewar kasar a Limbe da ke a yankin Ingilishi na Kamaru inda mutane biyar suka mutu.