1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Karin takunkumi ga Koriya ta Arewa

Lateefa Mustapha Ja'afar
February 7, 2018

Kasar Amirka ta sha alwashin sake kakabawa Koriya ta Arewa takunkumi bisa shirin Koriyan na nukiliya.

https://p.dw.com/p/2sI3R
Mataimakin shugaban ksar Amirka Thomas Pence
Mataimakin shugaban ksar Amirka Thomas PenceHoto: Reuters/A. Schalit

Mataimakin shugaban kasar Amirka Mike Pence ne ya yi wannan alwashin, inda ya ce za su kara tsaurara takunkumi ga Koriya ta Arewan. Pence ya nunar da hakan ne bayan da ya tattauna da Firaministan Japan Shinzo Abe a birnin Tokyo, yana mai cewa Amirka da kawayenta za su kara daukar matakan kakaba tsauraran takunkumai ga Koriya ta Arewan bisa ci gaba da take yi da shirinta na nukiliya, inda ya ce har matakan soja za su dauka idan bukatar hakan ta taso.