1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kame-kamen 'yan adawa a Masar

November 28, 2014

Hukumomin tsaro a Masar sun kama mutane fiye da dari kafin wata zanga-zangar da magoya bayan tsohon shugaban kasar Mohamed Morsi suka kira a wannan Jumma'a.

https://p.dw.com/p/1Dwan
Hoto: picture-alliance/AA/M. Hossam

Ofisfin ministan tsaron cikin gidan kasar ta Masar ne ya sanar da kame mutane akalla 107, kafin zanga-zangar nuna kin jinin gwamnati da suka shirya gudanarwa a wannan Jumma'a. Tun dai kifar da gwamnatin Mohamed Morsi, sabbin hukumomin kasar ta Masar ke shan gwagwarmaya tare da neman toshe duk wata kafa ta zanga-zanga ga magoya bayan tsofon shugaban kasar, inda ake zargin su da shirya zanga-zanga mai muni gami da tashe-tashen hankula.

Mawallafi: Salissou Boukari
Edita : Umaru Awal