1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kamaru ta fara tura sojinta kan iyakarta da Najeriya

May 27, 2014

Gwamnatin Kamaru ta fara jibge dakarunta a yankin arewacin ƙasar kan iyakarta da Najeriya domin yaƙi da Ƙungiyar Boko Haram.

https://p.dw.com/p/1C7sQ
Kamerun Präsident Paul Biya Archivbild 30.01.2013
Hoto: Patrick Kovarik/AFP/Getty Images

Wani babban jami'in tsaro ,ya ce an fara tura dakarun ne, a yau waɗanda suke isa zuwa kan iyakar gungu-gungu, wanda kuma ya ce sun shirya tura dakaru dubu ukku. Aikewa da dakarun da ƙasar ta Kamaru ta yi wacce ta raɓa iyaka mai tsawon gaske da Najeriya,na zuwa ne a ƙasa da makonnin biyu da kammala taron Faransa, wanda ya duba hanyoyi da za a bi don magance matsalar ta rashin tsaro a yanki.

Wacce ke zaman babbar barazana ga ƙasashen yankin waɗanda suka haɗa da Nijar da Kamaru da Chadi da kuma Benin. A wani labarin kuma a yau an ba da rahoton cewar 'yan Ƙungiyar ta Boko Baram; sun kashe jami'an tsaro 25 a garin Buni Yadi na Jihar Yobe.

Mawallafi : Abdourahamane Hasane
Edita : Zainab Mohammed Abubakar