An kai hari kan 'yan sanda a Kamaru
July 1, 2018Talla
Shaidun gani da ido dai sun ce an ragargaza wani bangare na ofishin 'yan sandan da ke unguwar Munya, inda suka ce an ji karar harbe-harbe a cikin daran Asabar wayewar garin wannan Lahadin da harin ya afku. Wasu 'yan awaran kasar ta Kamaru sun ce wani gungun mayaka ne masu rajin ganin an raba kasar ta Kamaru suka kai wannan hari, sai dai gwamnatin ta Kamaru ba ta ce uffan ba kan lamarin.
Hare-hare gami da sace mutane,da ma kashe-kashe, ya zama ruwan dare gama duniya a yankin na Kamaru da ake magana da Turancin Ingilishi, inda sojojin kasar ke yakar mayaka 'yan aware. Kawo yanzu dai sojojin kasar ta Kamaru sama da 80 ne suka mutu sakamakon wannan rikici, sannan kuma an kashe daruruwan fararen hula.