1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaben tsakiyar wa'adi na Amirka

Abdourahamane Hassane
November 7, 2022

Al'ummar Amirka na shirin kada kuri'a a zaben tsakiyyar wa'adi cikin wani yanayi na yakin da Ukraine ke yi da Rasha da ka iya yin tasiri a zaben.

https://p.dw.com/p/4JAgQ
USA Washington | Jahrestag Sturm auf das Kapitol 2021 | Joe Biden, Präsident
Hoto: Greg Nash/AFP/Getty Images

Zaben wanda ake gani zai kasance zakaran gwajin dafi ga jam'iyyar Democrate ta Joe Biden na fuskantar babban kalubale daga jam'iyyar Republicain ta Donald Trump wanda ke da niyar sake tsayawa takara a zaben shugaban kasa na tafe. Mutane kamar miliyan 250 ake sa ran za su kada kuri'a domin zaben 'yan majalisar wakilai 435 a tsawon wa'adin  mulkin shekaru biyu. A rana ta karshe ta yaki neman zabe Joe Biden ya jagorancin taron gangami a Jihar maryland da ke a gabashin Amirka kusa da Washington. Masu aiko da rahotanni na cewar yakin da ake yi tsakanin Rasha da Ukraine na iya yin tasiri a zaben.