1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kalubalantar salon tafiyar da mulki a Nijer

July 10, 2013

Babbar jam'iyyar adawa a Nijer ta zargi gwamnatin kasar da cin hanci da rashawa da kuma rashin iya gudanar da mulki.

https://p.dw.com/p/195vY
Titel: Seini Oumarou, Vorsitzender der Partei MNSD im Niger Schlagworte: Niger, Oumarou, Opposition, MNSD Wer hat das Bild gemacht?: offizielles Bild (MNSD) Wann wurde das Bild gemacht?: 2013 Wo wurde das Bild aufgenommen?: Niamey, Niger Bildbeschreibung: Bei welcher Gelegenheit / in welcher Situation wurde das Bild aufgenommen? Wer oder was ist auf dem Bild zu sehen? Seini Oumarou ist Vorsitzender der Partei MNSD-Nassara (Mouvement National de la Société de Développement ) und seit April 2011 Oppositionsführer im Niger. Zuvor hatte er in der Stichwahl um die Präsidentschaft gegen Mahamadou Issoufou verloren.
Hoto: MNSD

Jam'iyyar MNSD Nassara mai adawa a jamhuriyar Nijer ta kira taron manema labarai a wannan Larabar (10.07.13) inda ta kalubalanci halin sakacin da gwamnatin jamhuriya ta bakwai take nunawa a fannoni da dama na tafiyar da mulkin kasa, kama daga mataki na tsaro zuwa almubazzaranci da dukiyar kasa, da ma rashin iya tafiyar da mulki.
Malam Ali Sabo, mataimakin shugaban jam'iyyar MNSD Nassara
reshen jihar Maradi  shi ne ya jagoranci wannan taro, kuma ya tabo matsalolin da kasar ke fuskanta
"Akwai abubuwa da dama fiye da 100 da muke iya bayyana muku da suka yi da bai kamata ba, kuma ba mu zagesu ba, amma mun san rashin kulawarsu ce ta janyo wadannan matsaloli kuma muka ce a kula, sannan batun arzikin kasa kamar man fetur, kamar karfen Uranium  duk kokowar da muka yi a baya tare da kamfanoni na waje sun byi watsi da su inda kowa ke kokarin cika aljihunsa maimakon yayi kokawa dan ci-gaban kasa domin shi kishin kasa abu ne mai wuya, dan haka kyawon da yayi kishin kasarsa."

This photo taken on June 1, 2013, shows soldiers standing guard at the entrance of the main prison in Niamey. Inmates in Niamey's main prison killed two guards on June 1, officials said, a week after twin suicide bombings claimed 20 lives in the west African country. Three inmates charged with terrorist offences tried to had break out of the prison, prosecutor Ibrahim Wazir Moussa said on state television. AFP PHOTO / STRINGER (Photo credit should read STR/AFP/Getty Images)
Hoto: STR/AFP/Getty Images

Tsadar rayuwa da matsalar tsaro a Nijer
Da suke magana a fannin jin-dadin rayuwar al'umma , inda suka ce komai ya tsaya cik, rayuwa ta yi tsada sannan ga batun tsaro da ya kasance ana takura wa al'umma cikin kasa sannan da batun wasa da dukiyar kasa. Laouali Amadou, mai Zoumbou shi ne mataimakin shugaban jama'iyyar ta MNSD Nassara reshen jihar Dosso, yayi nashi tsokaci:

Yace "Wajan harkar tsaro magabatan na yanzu ba su dauki matakkan da ta kamata su dauka ba, kawai sai kada mutane na sanya tanonuwa a wurare, tare da sanya jami'an tsaro a gidajen su domin kariyarsu, abun da ya kamata, ita matsala tun kafin ta shigo ya kamata a ce an ganota kuma a dauki matakin maganceta musamman ma a fannin tsaro, mun gani lalle ayyukan da ake ana sanya kudade da dama a kansu. Misali, hanyar da za ta ci miliyan 15,000.00 sai ka ga anyi ta miliyan 30,000.00 a wannan gwamnati."
Tsawon awowi da dama ne 'yan adawar suka dauka suna baiwa 'yan jarida bayanai kan halin da kasar ta shiga na rashin tabbas a cewar su wanda kuma suka yi kira ga magabatan wannan kasa da su yi amfani da jan-hankalin da suke yi musu na gyara kayanka, amma ga bisa dukkan alamu a cewarsu, shiru ne har yanzu.

NIAMEY, Feb. 9, 2011 () -- File photo taken on Jan. 31, 2011 shows Nigerian presidential candidate Mahamadou Issoufou of the PNDS-Tarayya party speaking to the press after voting at a polling station in Niamey, capital of Niger. Leaders of Nigerian Democratic Movement for African Federation declared on Feb. 9 that they will support Issoufou during the run-off of the presidential election. Candidates Mahamadou Issoufou of the PNDS-Tarayya party and Seini Oumarou of the MNSD-Nassara have emerged as the No. 1 and No. 2 in the Dec. 31 presidential election and will enter the second round, which will be held on March 12. (/Ding Haitao) (wjd)
Shugaba Issoufou, na NijerHoto: picture alliance/Photoshot

Martanin jam'iyyar PNDS dake mulki a Nijer
Sai dai daga nashi bangaren, mai kula da yada labarai na jama'iyyar PNDS Tarayya mai mulki, Malam Iro Sani, cewa yayi, wannan zargi nasu shaci-fadi ne, kuma suna yinshi ne dan kar a ce basu ce ba:

Yace "Wannan sanarwar tasu sanarwa ce ta wanda ba shi da wani abun fadi domin shaci-fadi ne kawai, ba dan sun fito sun fadi abun da suke so, ba zai zama gaskiya domin kowa na iya shiga cikin dakinsa ya sha fura ya fito ga fili yayi maganarsa yadda ya ga dama. Demokradiya haka ta gada amma gaskiyar lamarin shi ne kowa ya zo cikin wannan kasar ya san anyi aiki kuma aiki ne da yafi na tsawon shekaru goma da MNSD tayi tana mulki.
A halin yanzu dai, hankulan al'umma a wannan kasa ta jamhuriyar Nijer, sun karkata wajen jiran fitowar sabuwar gwamnati da ake rade- raden fiddowa wadda tun bata zoba ake jiran ta taka rawar gani sosai dan magance wasu matsalolin da ake ganin ta yanzun bata shawo kansu ba.

Mawallafi : Salissou Boukari
Edita        : Saleh Umar Saleh