Kaddamar da bincike a kan kisan kimanin mutane 10 a Abuja
September 24, 2013Al'amura na kara lalacewa kuma fushi na al'umma na karuwa game da kisan wasu matasa kusan 10 da ake zargin jami'an tsaron cikin gida na SSS da yi a cikin makon jiya, da kuma ke ci gaba da tada hankali tsakanin sarki dama talakawan kasar ta Najeriya.
Na baya baya dai na zaman majalisar dattawan kasar da ta nuna bacin ranta bisa kisan, sannan kuma ta kafa wani kwamitin bincike da nufin tabbatar da gaskiyar abin da ya faru.
A wata muhawarar da ta dauki tsawon lokaci ana tafkawa dai, ra'ayi ya zo daya a tsakanin dattawan da suka ce tayi baki ta kuma baci ga batun cin zarafi na farar hula a sassa daban daban na kasar.
Senata Kabiru Ibrahim Gaya dai na zaman dan majalisar dattawan aaga Kano, kuma a cewar sa sun bai wa kwamitocin kare hakkin bil'adama da na Sharia'ar ta da su kaddamar da cikakken bincike a mika rahoto a cikin mako guda kacal.
Makomar sakamakon binciken rigingimu a Najeriya
To, sai dai kuma kokarin bincike na gaskiya ko kuma kokarin kwantar da hankali dai, a baya majalisar ta kai ga kafa jerin kwamitoci a irin wannan matsala a Baga da Bama da Maiduguri da ma sassa daban daban na arewacin kasar, ba tare da yin wani tasiri ga kokarin sauya ko in kular jami'an tsaron tarayar Najeriyar ba.
Akwai ma dai tsoron yiwuwar cin shirwar mallam game da sakamakon binciken da ma kila matakan da 'yan kasar ke fatan gani cikin kasa da nufin adabo da izgilancin da ya sha sanadiyyar asarar rayuka a tituna da unguwanni na fararen hula.
To sai dai kuma a cewar Senata Sahabi Ya'u da tun da farko ya gabatar da bukatar binciken dai, babban aikin majalisar bai wuci mika wa bangaren zartarwar kasar sakamkon binciken domin cika nasu bangare na dokokin kasar.
To, sai dai ko ya zuwa yaushe ne dai al'ummar kasar ke shirin sanin gaskiyar abin da ya faru a unguwar ta Apo dai, tuni dai wata gaskiya mai daci a siyasar kasar ta fara baiyyana tare da shugaban tarayyar Najeriyar Goodluck Ebele Jonathan, ya shaida wa wani taro na 'yan kasar a birnin New York cewa fa lalle fa karen nan yana shirin sunsuna takalmin mulki a kasar.
Yiwuwar takarar shugaba Jonathan a zaben 2015
Jonathan din da yanzu haka ke cikin tsakiyar wani rikicin cikin gidan da ke neman raba kan jam'iyyar sa ta PDP gida biyu dai, ya ce kundin tsarin mulkin kasar ya mika masa 'yancin mulki na shekaru takwas ba wai ba inke.
Abin kuma da ke zaman alamun ta lalace a cikin sulhun dake tsakanin 'ya'yan sabuwa da tsohuwar PDP amma kuma a fadar Barrister Abdullahi Jalo da ke zaman mataimakin kakakin PDP har yanzu da sauran fata.
Taba 'yanci ko kuma aiken sako dai, tuni masu adawa da takarar ta shugaban kasar suka fara karatun ganganci kuma wauta ga shugaban, na tuni wata takarar da ke iya daukar wa'adin mulkinsa zuwa shekaru sama da tara karkashin tsarin da a cewar Dakta Umar Ardo, wani masani na siyasa ya yarje masa shekaru takwas kacal.
Babban kalubale ga masu shari'ar dai na zaman ko shekara daya da kwanaki 23 na kama mulkin Jonathan na zaman cikin cikakken wa'adinsa ko kuma a'a.
Mawallafi : Ubale Musa
Edita : Saleh Umar Saleh