1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

John Kerry zai tattauna da shugabannin Isra'ila da Falasɗinu

March 31, 2014

Sakataran harkokin wajen Amirka John Kerry ya fara yin wata ziyara aiki a Yankin Gabas ta Tsakiya

https://p.dw.com/p/1BZJm
Paris Treffen Außenminister Ukraine 5.3.2014 John Kerry
Hoto: Reuters

Kerry wanda ya isa a yau birnin Tel-Aviv, an shirya zai gana da firaminsta Isra'ila Benjamin Netanyahu a birnin Ƙudus, da kuma jagoran falasɗinawa Mahamud Abbas a Ramallah, kafin ya isa a Brussel a gobe Talata idan zai halarci taron Ƙungiyar NATO.

Isra'ila dai ta ƙi ta saki wani rukunin na ƙarshe na fursunan Falasɗinu a ranar Asabar da ta gabata kamar yadda aka tsara a tattaunawar ta farfaɗo da zaman lafiya a yanki Gabas ta Tsakiyar. Tana mai cewar za ta sake sune kawai, idan Falasɗinu ta amince a ƙara tsawaita wa'adin tattaunwar ta gaba da gaba da nufin samun zaman lafiya wadda wa'adinta ke kawo ƙarshe a ranar 29 ga watan Afrilu.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Mohammad Nasiru Awal