1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

John Kerry ya kai wata ziyarar ba zata a Bagadaza

Mohammad Nasiru AwalSeptember 10, 2014

Wannan ziyarar da ba a sanar tun farko ba, tana cikin rangadin kasashen yankin Gabas ta Tsakiya da yake yi da nufin hada karfi don yakar kungiyar IS.

https://p.dw.com/p/1D9sk
John Kerry mit Abadi in Bagdad
Hoto: Reuters/B. Smialowski

Sakataren harkokin wajen Amirka John Kerry ya kai ziyara Bagadaza babban birnin kasar Iraki don tattaunawa da shugabannin kasar. Ba a dai sanar da kai wannan ziyara ba da ke cikin rangadin kasashen yankin Gabas ta Tsakiya da Kerry din ke yi da nufin samun goyon bayan shugabannin yankin a yakin da ake yi da mayakan kungiyar IS mai da'awar kafa daular Musulunci a Iraki da Siriya. Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Amirka ya ce Kerry zai gana da sabon Firaministan Iraki Haidar al-Abadi da shugaban kasa Fuad Massum da ministan harkokin waje Ibrahim Jafari sai kuma shugaban majalisar dokoki Salim al-Jaburi. Wannan ziyara a Bagadaza ta zo ne sa'o'i kalilan gabanin wani jawabi da Shugaba Barack Obama zai yi wa al'ummar Amirka inda zai gabatar da manufofin yakinsa da kungiyar IS.