An fara janye dakarun Chadi daga Jamhuriyar Nijar
October 13, 2017Talla
Hukumomin Jamhuriyar Nijar sun tabbatar da fara janye dakarun kasar Chadi daga Jamhuriyar Nijar wadanda suke aikin samar da tsaro sakamakaon rikicin Boko Haram da ya ritsa da wasu kasashe na Afirka wadanda suka hada da Najeriya, da Jamhuriyar Nijar, da Kamaru gami da Jamhuriyar Nijar.
Ana sa ran amfani da sojojin na Chadi wajen karfafa tsaro musamman kan iyakar kasar ta Chadi da kuma Libiya, inda ake samun matsaloli na tsaro gami da masu safarar mutane masu neman shiga kasashen Turai. Hukumomin na Jamhuriyar Nijar sun ce tun watanni shida da suka gabata aka fara matakin na yanje sojojin Chadi musamman daga yankin Diffa wanda ya gamu da hare-haren tsageru masu nasaba da Boko Haram.