1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Angola: Jana'izar Jose Eduardo dos Santos

Ramatu Garba Baba MAB
August 28, 2022

Wasu daga cikin shugabanin kasashen Afirka sun isa birnin Luanda don yi wa tsohon shugaban kasar Angola Jose Eduardo dos Santos bankwanan karshe.

https://p.dw.com/p/4G9g6
Angola - Trauerfeier für José Eduardo dos Santos
Hoto: António Cascais/DW

Shugabanin kasashen Afirka da dama ne ke halatar jana'izar tsohon shugaban kasar Angola Jose Eduardo dos Santos. An shirya yi wa marigayin da ya kwashi kusan shekaru arba'in kan madafun ikon kasar, faretin ban girma a yayin jana'izar da ke gudana a wannan Lahadin.

A watan Yulin da ya gabata, Dos Santos ya mutu bayan ya sha fama da rashin lafiya a wani asibiti da ke birnin Barcelona na kasar Spaniya da ke yankin Turai. Yan Angola na yi wa Dos Santos bankwanan karshe, mako guda bayan da suka sake zaben shugaba mai ci Joao Lourenco na jam'iyyarsa ta MPLA da ta shafe kusan shekaru hamsin tana mulkin kasar ta Angola.