1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus za ta sayar wa Saudiyya da makamai

Gazali Abdou Tasawa
September 20, 2018

Gwamnatin Jamus ta ba da izinin sayar da makamai ga wasu kasashen yankin Gabas ta Tsakiya da suka hada da kasar Saudiyya.

https://p.dw.com/p/35D9L
Deutsche Firmen verdreifachen Rüstungsexporte
Hoto: picture-alliance/dpa/T. Tinazay

Kamfanin dillancin labaran kasar ta Jamus ya ruwaito cewa ministan tattalin arzikin kasar Peter Altmaier a wata wasikar da ya aika wa kwamitin kula da tattalin arziki a majalisar dokokin kasar ya tabbatar da amincewar gwamnatin na sayar wa da kasar ta Saudiyya makamai.. 

A cikin wasikar minista Altmaier ya bayyana cewa Jamus za ta sayar wa kasar Saudiyya da wasu na'urori hudu na girka makaman atilare. Yarjejeniyar da jam'iyyun da ke kawancen mulki a kasar ta Jamus ta cimma a baya ta tanadi haramta sayar da makamai ga kasar Amirka da kuma Saudiyya kasancewa suna da hannu a yakin kasar Yemen. Sai dai kuma Saudiyya ta kasance babbar aminiyar kasashen yamma a fagyen yaki da Kungiyar IS a kasar Siriya.