1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Agaji ga 'yan gudun hijirar Moria

Binta Aliyu Zurmi
September 11, 2020

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta sanar da aniyarsu na daukar kananan yara 150 daga cikin wadanda gobarar sansanin yan gudun hijira mafi girma a nahiyar Turai na Moria da ke kasar Girka ya rutsa da su. 

https://p.dw.com/p/3iLZo
Griechenland Lesbos | nach Brand im Moria-Lager
Hoto: AFP/L. Gouliamaki

Wannan na zuwa ne bayan da Firaiministan kasar Girkar ya bukaci taimako daga kasashen kungiyar EU.
Har wayau Jamus ta yi alkawarin kyautata rayuwar wadannan mutanen tare da samar musu matsuguni mai kyau.

Ministan harkokin cikin gidan Jamus Horst Seehofer ya sanar a wannan rana ta Juma'a cewar kasashen EU goma za su dauki kananan yara kimanin 400. Kungiyar ta tarayar Turai na shirin fidda sabbin yarjejeniya game da 'yan gudun hijira da ma yan ci-rani a nahiyar.