1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus ta yaba da matakin Amirka

February 5, 2021

Gwamnatin Jamus ta yi maraba da hukuncin shugaban kasar Amirka na dakatar da rage dakarun Amirka a kasarta, inda shugaban yake mai cewa dakarun dai bukatu ne na kasashen biyu.

https://p.dw.com/p/3owsC
Kanzlerin Angela Merkel und Präsident Trump
Hoto: picture-alliance/AP Photo/E. Vucci

A wani bangare na sake fasalin manufofin kasashen waje da na tsaro da aka gabatar a ranar Alhamis, Biden ya sanar da dakatar da shirye-shiryen wanda ya gada wato tsohon shugaba Donald Trump na rage kasancewar sojojin Amurka a Jamus, ginshikin tsaron NATO tun farkon fara yakin cacar baki.

Ana ganin matakin na tsohuwar gwamantin Shugaba Trump na da nasaba da dangantaka mai tsami tsakaninsa da shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel da kuma yawan korafin da yake yi na cewa kasasahen Turai da suka fi karfin tattalin arziki na kasashe kudi kalilan kan sha'anin tsaro.