1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus ta karfafa amfani da manhajar yaki da corona

June 20, 2020

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta bayar da shawarar amfani da damar da aka samu ta sabuwar manhajar da aka kirkiro mai yaki da yaduwar cutar corona tsakanin jama'a.

https://p.dw.com/p/3e5HZ
Würzburg | Frau mit Mundschutz guckt auf Ihr Handy
Hoto: picture-alliance/HMB Media/H. Becker

A wannan makon ne dai aka kaddamar da sabuwar manhajar wadda ake saukewa a wayoyin hannu, kuma manhaja ce mai karfin adana bayanan da ta tattara tare da nuna mai cutar nan take. A cewar Angela Merkel amfani da 'yan kasar Jamus za su yi da sabuwar manhajar, shi ne zai taimaka wajen samar da sakamakon da ake bukata game da cutar don daukar mataki.

Manhajar na kuma iya shaida wa sauran wadanda ke da ita a wayoyinsu, matsayin duk wanda ya gitta kusa da su, masalan idan ya kamu. Gwamnatin Jamus dai ta tsaya kan tabbatar da tsarin manhajar, bai kai ga tattara bayanan sirri na wadanda za su yi amfani da ita ba.