1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus da Rasha na yunkurin hana farmakin Idlib

Ramatu Garba Baba
September 14, 2018

Batun hana kai farmakin kwato birnin Idlib daga hannun 'yan tawayen Siriya zai kasance muhinmin batu da a wannan Juma'a, ministan harkokin wajen Jamus Heiko Maas zai tattauna da takwaransa na Rasha Sergei Lavrov.

https://p.dw.com/p/34qFO
Außenminister Maas in Russland
Hoto: Getty Images/AFP/Y. Kadobnov

Mista Maas ya ce, kowa na sane kan hadarin da dubban jama'a za su fada ciki, muddun aka kai wannan farmaki a kokarin kwace ikon birnin da gwamnatin shugaba Bashar al-Assad mai samun goyon bayan kasashen Rasha da Iran da Turkiya ke yunkurin yi.Ministocin biyu za su gana a yau a birnin Berlin.

Majalisar Dinkin Duniya da kasashe masu fada a ji, suna ci gaba da yin gargadin kaucewa aukuwar abin da suka kira, babban bala'i ga dubban fararen hula da ke yankin, sun ce kuskure ne mai girman gaske yin hakan, ganin rayukan da ka iya salwanta.

Gwmantin Siriya dai ta tura dubban sojoji yankin, inda za su yi anfani da karfi don fatatakar 'yan tawayen da aka yi kiyasin sun kai dubu talatin. Rasha na daga cikin kasashen da ke marawa gwamnatin Assad baya don ganin ta sami galaba a rikicin kasar na sama da shekaru bakwai.