1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jammeh ya fara gudun hijira a kasar Equatorial Guinea

Zainab Mohammed Abubakar
January 22, 2017

Tsohon shugaban Gambiya Yahya Jammeh ya fice daga kasar da ya yi mulki na tsawon shekaru 22, a wani mataki na warware rikicin siyasa da kasar ta yammacin Afirka ta tsinci kanta a ciki.

https://p.dw.com/p/2WCrK
Ex-Präsident Jammeh verlässt Gambia
Hoto: Picture-Alliance/dpa/J. Delay

Mutumin da tun farko ya ki sauka daga mulki duk da kaye da ya sha a zaben ranar 1 ga watan Disamba, Jammeh ya yi sanadiyyar tayar da jijiyar wuya da yunkurin daukar matakin soja, da nufin tilasta shi bawa sabon shugaban kasar Adama Barrow madafan iko.

Tsohon shugaban na Gambiya tare da rakiyar Shugaba Alpha Conde na Guinea sun bar birnin Banjul a wani karamin jirgin sama zuwa Conakry babban birnin Guinea kana daga bisani ya shige kasar Equatorial Guinea, inda zai yi zaman gudun hijira, a cewar shugaban kungiyar ECOWAS Marcel Alain de Souza a birnin Dakar.