1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

CDU za ta zabi sabon shugaba

Abdul-raheem Hassan
February 24, 2020

Sasanta rikicin cikin gida a jam'iyyar CDU zai ba ta damar gyara zaman tinkarar matsanancin ra'ayin rikau da ke neman mamaye siyasar kasar.

https://p.dw.com/p/3YGvi
Berlin CDU Pressekonferenz Annegret Kramp-Karrenbauer
Hoto: picture-alliance/dpa/B. von Jutrczenka

A yau ne ake sa ran jam'iyyar CDU ta 'yan mazan jiya a Jamus za ta bayyana sabon shugabanta bayan rudanin da jam'iyyar ta shiga a baya kan wanda zai gaji Shugabar gwamnati Angela Merkel da ke shirin barin mulki a 2022.

Ana sa ran a wannan litinin tsohuwar shugabar jam'iyyar Annegret Kramp-Karrenbauer za ta bayyana matsayarta bayan yin murabus daga shugabacin jam'iyyar a watan Janairu.