1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamiyun adawa a Jamus sun neman bincike akan leken asiri a Iraqi

January 17, 2006
https://p.dw.com/p/BvBq
Farfesa Dr. Ingo Rechenberg, shugaban cibiyar nazarin kwaikwayo da halitta, wato BIONICS, a jami'ar kimiyya da fasaha ta birnin Berlin.
Farfesa Dr. Ingo Rechenberg, shugaban cibiyar nazarin kwaikwayo da halitta, wato BIONICS, a jami'ar kimiyya da fasaha ta birnin Berlin.

Jamiyun adawa 3 na nan Jamus,da alama suna shirin mika bukatarsu ta gudanar da bincike akan harkokin jamian leken asiri na Jamus a kasar Iraqi ,a lokacin mamayar Iraqin a 2003.

Hukumar leken asiri ta Jamus din BND ta tabbatar da cewa wasu jamianta guda biyu sun kasance a birnin Bagadaza a lokacinda Amurka ta fara jefa bama bamai a Iraqi,amma ta karyata zargi dake cewa ta taimaka gano wasu wurare da dakarun Amurka suka dagargaza da bama bamai.

Sai dai kuma jamiyar hadaka dake mulki tayi watsi da kira da akeyi na gudanar da bincike akan wannan zargi.