1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jama'a na cikin murna a Timbuktu

January 29, 2013

Murna ta kaure dangane da yadda sojojin Faransa da na ƙasashen Afirka da ke tallafa wa sojojin Mali suka sake ƙwacce birnin daga cikin hannun masu kishin addini.

https://p.dw.com/p/17TGL
Malian soldiers wait at a checkpoint near Sevare on January 27, 2013. French-led troops were advancing on Mali's fabled desert city of Timbuktu on Sunday after capturing a string of other towns in their offensive against Islamist militant groups in the north of the country. Meanwhile, African leaders meeting in the Ethiopian capital were discussing scaling up the number of African troops to join the offensive, after the African Union's outgoing chief admitted the body had not done enough to help Mali. AFP PHOTO / FRED DUFOUR (Photo credit should read FRED DUFOUR/AFP/Getty Images)
Hoto: Fred Dufour/AFP/Getty Images

Rahotanni daga birnin Timbuktu na cewar jama'a na ci gaba da kasancewa cikin farin ciki, bayan da sojojin Faransa da ke dafa wa dakarun Mali suka sake ƙwato birnin daga hannun masu kishin addini waɗanda suke riƙe da shi kusan watanni da dama.

A lokacin da sojojin na Faransa da na Mali da kuma na Tarrayar Afirka ke tinkarar garin na Timbuktu ɗaruruwan jama'a ne suka yi lale marhabin da su, inda wani mazaunin garin ya ke cewar a da, suna cikin tsoro da fargaba, ba su samun yin barci, amma yanzu ya ce sun samu kan su. Masu kishin addinin gabannin ficewar su ,daga birnin sai da suka ƙwana duban littattafai na tarihi a gidan adana kayan tarihi na garin.Yanzu haka kuma a kwai rahotannin da ke cewar 'yan tawayen sun sulale cikin jama'ar birnin.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Saleh Umar Saleh