1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mayakan Kungiyar IS sun kai hari kan fararen hula

Ramatu Garba Baba
February 18, 2023

Ana zargin mayakan Kungiyar IS da hannu a wani kazamin harin kwanton bauna da ya rutsa da wasu mafarauta da sojojin kasar Siriya a yankin Homs.

https://p.dw.com/p/4NgKv
Hoto: DELIL SOULEIMAN/AFP

Kafafofin yada labarai na kasar Siriya sun tabbatar da mutuwar mutum akalla 68 da suka ce sun mutu ne a sakamakon wani harin kwanton bauna da ake zargin mayakan IS da kai wa. Fararen hula 61 da suka kasance mafarauta da kuma sojoji bakwai ne suka gamu da ajalinsu a sakamakon harin.

Harin na birnin Homs a daren Jumma'ar da ta gabata, ya kasance hari mafi muni da mayakan ke kai wa yankin Homs a fiye da shekara guda a kasar da rikici ya daidaita. Kawo yanzu babu wata sanarwa daga bangaren mayakan na IS da ba sa wata-wata wajen sanar da daukar alhakin kai hare-harensu.