1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran ta yi watsi da zargin Saudiyya

Abdul-raheem Hassan
May 31, 2019

Gwamnatin Iran ta ce kasashen yankin Gabas ta Tsakiya na mata zargi mara tushe kan ta'addanci a taron koli na gaggawa da kasashen ke yi a Makka.

https://p.dw.com/p/3JWdI
Tunesien Gipfel der Arabischen Liga in Tunis
Hoto: Getty Images/AFP/F. Belaid

Saudiyya na neman hadin kan kasashen Amirka da Isra'ila da sauran kasashen duniya domin dakatar da Iran daga yunkurin yi wa yankin Gabas ta tsakiya barazana.

Sarki Salman bin Abdul'azeez al-Sa'ud ya Iran da tallafawa ta'addanci tare da neman kaiwa jiragen dakon man ta harin, amma kasar Iran ta musanta wannan zargi tare da cewa yunkuri ne kawai na neman yi mata taron dangi. A baya-bayannan dai Amirka na cigaba da jibge tannkokin yaki da sojoji a yankin Gabas ta tsakiya a wani mataki na yi wa Iran barazana daukar wani mataki da zai kai ga tada yaki.