1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Kanu ya bukaci kotun Najeriya ta wanke shi

January 19, 2022

A cikin makon nan ne dai gwamnatin Najeriya ta kara sabbin laifukan, cikinsu kuwa har da zargin Kanu da  ta'addanci. Galibin zarge-zargen na da alaka da kalaman da Kanun ya yi a 2018 a gidan rediyonsa, Radio Biafra.

https://p.dw.com/p/45nN5
Karte Nigeria Biafra
Hoto: DW

Jagoran haramtacciyar kungiyar IPOB mai rajin ballewa daga Najeriya Nnamdi Kanu ya musanta sabbin laifuka takwas da gwamnatin Najeriya ke zargin shi da aikatawa a zaman kotun da aka yi a wannan Laraba.

A cikin makon nan ne dai gwamnatin Najeriya ta kara sabbin laifukan, cikinsu kuwa har da zargin Kanu da  ta'addanci da tunzura jama'a. Galibin zarge-zargen na da alaka da kalaman na Kanu wanda ke da takardar zama dan kasar Burtaniya ya yi a shekara ta 2018 a gidan rediyonsa mai suna Radio Biafra. 

Sai dai kotun da ke Abuja ta dage ci gaba da shari'ar zuwa ranar 14 ga watan Fabrairu, a yayin da kotun za ta ci gaba da nazarin lauyoyin Kanu na cewa a yi watsi da zarge-zargen da gwamnati ke masa.


A gefe guda wata kotu da ke jihar Abia a kudancin Najeriya ta umurci gwamnatin kasar da ta biya Nnamdi Kanu Naira miliyan dubu daya, a matsayin diyya saboda samamen da jami’an tsaro suka kai gidan mahaifinsa cikin watan Satumbar 2017.