1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

ICC ta ɗage shari'a shugaban ƙasar Kenya

October 31, 2013

Babbar kotun duniya da ke hukunta manyan laifukan yaƙi ta ce za a yi shari'ar ta Uhuru Kenyatta a ranar biyar ga wata Febrairu na shekara ta 2014.

https://p.dw.com/p/1A9tU
Kenya's President Uhuru Kenyatta makes his statement to the nation at the State House in Nairobi on September 22, 2013, following the overwhelming numbers of casualties from the Westgate mall shooting in the Kenyan capital. Kenyan President Uhuru Kenyatta said Sunday a nephew and his fiancee were among the 59 people confirmed killed in an ongoing siege in an upmarket shopping mall by Somali militants. AFP PHOTO / JOHN MUCHUCHA (Photo credit should read John Muchucha/AFP/Getty Images)
edeHoto: John Muchucha/AFP/Getty Images

Tun farko an shirya za a gudanar da zaman shari'ar ne a ranar 12 ga watan Nuwamba da ke kamawa a gobe,to amma kotun ta ce lauyoyin da ke kare shugaban ƙasar suka buƙaci a ɗage zaman.

Hakan kuwa ya biyo bayan hare-haren da aka kai a wata cibiyar kasuwancin ƙasar ta Kenya domin bai wa shugaban damar fiskantar lamarin. Ana tuhumar shugaban na Kenya da matamakinsa William Ruto da laifin haddasa tashin hakali da ya biyo bayan zaɓen shekarun 2007. Wanda a cikinsa mutane kusan dubu suka mutu yayin da wasu sama da dubu ɗari shida suka fice daga gidajensu.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman