1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za a sake komawa yin hulda tsakanin kasashen biyu

Abdourahamane HassaneJuly 19, 2015

Za a sake buɗe ofisoshin jakadanci tsakanin Amirka da Kyuba, bayan katseta da aka yi tun a shekarun 1961, saboda rashin zutuwar da aka samu tsakanin ƙasashen biyu.

https://p.dw.com/p/1G1MZ
US-Präsident Obama und Präsident Raul Castro beim Amerika-Gipfel in Panama
Hoto: Reuters/Jonathan Ernst

Nan gaba a daran yau Lahadi zuwa gobe Lititin aka shirya Amirka da Kuyba za su sake buɗe ofisoshin jakadancinsu a birnin Havana da Washington.

Wannan al'amari dai na zaman wani mataki na farko na sake farfaɗo da hulɗa diplomasiyya tsakannin ƙasashen biyu,bayan ganawar tarihi da aka yi a bara tsakanin shugaban Amirka Barack Obama da Raul Castro a Havana.

Hulɗar diplomasiyya tsakanin ƙasashen biyu ta tsinke tun a shekaru 1961 lokacin da Amirka ta ƙaƙabawa Kyuba takunkumin karya tattalin arziki saboda manufinta na siyasa waɗanda ta kamanta da na 'yan ta'adda.