1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hong Kong: An saki madugun 'yan fafutuka

Zulaiha Abubakar
September 9, 2019

Hukumomi a yankin Hong Kong sun saki madugun 'yan fafutukar tabbatar da dimukradiyya na yankin Joshua Wong wanda aka tsare shi.

https://p.dw.com/p/3PGKt
Joshua Wong Studentenführer der Protestbewegung in Hongkong
Hoto: Getty Images/AFP/A. Wallace

Kotu ce dai ta umarci da a saki Mr. Wong bayan wani takaitaccen zama da ta yi kan batun tsare shi inda ta ce bata ga hujjar kama shi da aka yi ba kamar yadda ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Jamus na DPA.

A wani sako da ya sanya shafinsa na Facebook a kan hanyarsa ta zuwa Jamus, Joshua Wong dan shekaru 22 da haihuwa ya ce zai cigaba da fafutuka wajen ganin lamura sun sauya a yankin na Hong Kong.

Tun cikin watan Yunin wannan shekarar ce dai Wong da magoya bayansa suka fara gudanar zanga-zanga a kan titunan yankin don nuna adawarsu da gwamnatin yankin kan batutuwa da dama ciki kuwa har da daftarin dokar nan da ya tanadi mika masu laifi ga China don yi musu shari'a.