1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin Isra'ila ya kashe gomman mutane a Gaza

September 21, 2025

Yayin da Isra'ila ke kara zafafa hare-harenta a Gaza, ta yi ikrarin cewa, Zirin Gaza ya zama maboyar mayakan kungiyar Hamas.

https://p.dw.com/p/50pqJ
Falasdinawa da suka rasa matsugunnansu na tsere wa zuwa arewacin Zirin saboda farmakin Isra'ila
Falasdinawa da suka rasa matsugunnansu na tsere wa zuwa arewacin Zirin saboda farmakin Isra'ilaHoto: Dawoud Abu Alkas/REUTERS

Ma'aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta ce, a kalla Falasdinawa 31 ne suka rasa rayukansu a wani harin da Isra'ila ta kai kan wasu gidaje a Zirin. Mutane da dama ne ke tserewa yayin da tankokin yakin Isra'ila ke kara matsawa kusa da garuruwan da ke dauke da jama'a.

Karin bayani: Isra'ila na ci gaba da rushe gidaje a Gaza

Isra'ila dai ta ce Gaza ce babbar matattarar maboyar Kungiyar Hamas, inda tun bayan zafafa farmakinta a farkon wannan watan, rundunar sojin kasar ta ke lalata ayarin gidaje da ta yi ikrarin mayakan Hamas na amfaani da su. Rundunar sojin Isra'ila dai bata ce komai dangane da mutuwar fararen hular ba, sai dai a cewarta, dakarunta sun kashe mayaka da dama.