1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin Boko Haram ya halaka mutane da dama

Ramatu Garba Baba
September 8, 2018

An samu asarar rayukan mutane da dama a sanadiyar harin da ake zargin mayakan kungiyar nan ta Boko Haram da kaiwa a garin Gudumbali da ke a jihar Borno a yankin Arewa maso yammacin Najeriya.

https://p.dw.com/p/34Xai
Nigeria Kano Selbstmordanschlag
Hoto: picture-alliance/dpa/Str

Rahotanni na cewa mayakan sun afka wa mazauna garin da ke a yankin Guzamala sanye da kayan sarki na sojoji inda suka bude wuta kan mazauna yankin dama sojojin da ke a bakin aikinsu. Jami'an tsaro da sauran al'umma sun tsere wa barin wuta a harin na ba-zata daga mayakan.

Wani ganau ya ce fararen hula da dama sun mutu kuma ba zai iya kayyade iyakacin jama'ar da suka rasa rayukansu daga harin na ranar Jumma'a ba, Dubban mutane ne suka kaurace wa gidajensu tun bayan aukuwar harin. Kawo yanzu babu karin bayani daga bakin mahukuntan kasar kan wannan harin.

A watan Yunin da ya gabata ne gwamnatin Najeriya ta umarci dubban 'yan gudun hijira na yankin Gudumbalin da suka tsere wa rikicin ta'addanci da su koma gidajensu bayan da ta ce an shawo kan Boko Haram. Yankin da ke a jihar Borno a Arewa maso gabashin Najeriya ya fuskanci munanan hare-hare inda aka tafka asarar rayuka da dukiya a sanadiyyar ayyukan kungiyar ta Boko Haram.