1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin bam ya ritsa da asibitin Mata a Siriya

Abdul-raheem HassanJuly 29, 2016

Jiragen yaki sun kai hari a asibitin Mata da ke Lardin Idlib a arewa maso kudancin Siriya.

https://p.dw.com/p/1JYiK
Syrien Krankenhaus Ärzte ohne Grenzen zerstört
Hoto: Reuters/A. Abdullah

Wani harin bam da jiragen yaki suka kai a lardin Idlib da ke arewa maso kudancin Siriya ya tarwatsa wani asibitin mata da kungiyar kula da kananan yara ta Save the Children ke kula da shi.

Kungiyar ta Save the Children dai ta yi kira ga dukkanin bangarorin da rikici da juna da su kai zuciya nesa don samun kai dauki ga dubban al'umma da ke cikin yanayi na bukata kana ta bukaci da kauracewa lalata gine-gine masu muhimmaci ciki kuwa har da asibitoci.

Kawo yanzu dai ba a kai ga tantance adadin asarar rayuka da aka samu ba, to amma a cewar kungiyar Syrian Obsarvatory for Human Rights da ke sa ido kan abubuwan da ke faruwa a kasar ta ce harin ya yi sanadiyar rasuwar mutane da dama.

Kungiyo kare hakkin bil'adama da ke Siriya, sun tabbatar da bayanai da ke cewa, dama an kai harin ne da nufin farautar wani dan jihadi da ya ziyarci matarsa da ta haihu a asibitin inda kuma aka hallaka shi.