1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hari kan Firimiyan Habasha

Ahmed Salisu
June 23, 2018

Rahotanni daga birnin Addis Ababa na cewar an samu fashewar wani abu a wajen wani gangami da firaministan kasar mai yunkurin kawo sauyi Abiy Ahmed ya ke halarta domin yin jawabi ga al'ummar kasar.

https://p.dw.com/p/308Gp
Äthiopien Kundgebung Premierminister Abiy Ahmed in Addis Ababa | Explosion
Hoto: Oromo Media Network

Fashewar abin wanda ake kyautata zatan bam ne, inda a jawabin da ya yi wa 'yan kasar bayan kai harin, firaminista Abiy Ahmed, ya ce harin ya yi sanadin mutuwar mutane da yawa kana ya jikkata mutane sama da 83, ko da yake daga baya a shafin twitter shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin kasar ta Habasha, ya musun ta cewa akwai wadanda suka mutu. A cewar firaministan, wasu makiyan zaman lafiya ne suka kai hari, amma ba su yi nasara ba. 

Wani ganau ya shaidawa Sashin Amharic na DW cewar ya ga mutane da damar gaske da suka jikkata, wanda aka kai su asibiti don yi musu magani kuma wasunsu na nan rai-kwakwai mutu-kwakwai, inda ya kara da cewa.

"Motar daukar marasa lafiya ta kwashi mutane da dama, da yawa daga cikinsu jina-jina kuma an kai su asibiti don yi musu magani. Wasu daga cikin wanda suka jikkatan na  cikin mawuyacin hali. Mutane na ta kokarin sanin abinda ya faru amma an ce mana bam ne ya tashi".