1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin 'yan bindiga a Mali

Lateefa Mustapha Ja'afarJanuary 20, 2016

Wasu 'yan bindiga dadi sun kai hari a kasar Mali tare da halaka jami'an jandarmomin kasar uku.

https://p.dw.com/p/1HhPH
Jami'an tsaron Mali na fuskantar kalubalen hare-hare
Jami'an tsaron Mali na fuskantar kalubalen hare-hareHoto: picture-alliance/AP

Wasu 'yan bindiga dadi sun kai hari kasar Mali tare da halaka mutane da dama. Wani shaidan gani da ido Moussa Saye ya ce maharan sun hallaka jami'an jandarma na kasar guda uku a yankin tsakiyar Mali. Saye wanda ke da zama a garin Mopti, ya ce ya na da 'yan uwa da ke zaune a kusa da inda aka kai harin na wannan Laraba. Dakarun kasar ta Mali sun tabbatar da faruwar harin, wanda suka ce dama yankin ya yi kaurin suna wajen samun tashe-tashen hankula daga tsagerun kungiyar "Macina Liberation Front", da ke da tsautsauran ra'ayin addini, wada kuma ta dauki alhakin kai hare-hare da dama cikin shekarar da ta gabata.