Harin 'yan bindiga a Mali
January 20, 2016Talla
Wasu 'yan bindiga dadi sun kai hari kasar Mali tare da halaka mutane da dama. Wani shaidan gani da ido Moussa Saye ya ce maharan sun hallaka jami'an jandarma na kasar guda uku a yankin tsakiyar Mali. Saye wanda ke da zama a garin Mopti, ya ce ya na da 'yan uwa da ke zaune a kusa da inda aka kai harin na wannan Laraba. Dakarun kasar ta Mali sun tabbatar da faruwar harin, wanda suka ce dama yankin ya yi kaurin suna wajen samun tashe-tashen hankula daga tsagerun kungiyar "Macina Liberation Front", da ke da tsautsauran ra'ayin addini, wada kuma ta dauki alhakin kai hare-hare da dama cikin shekarar da ta gabata.