Hari a birnin Leicester na Birtaniya
February 26, 2018Talla
'Yan sanda a Birtaniya, sun nesanta fashewa tare da rushewar wani gini da suka jikkata mutum shida a birnin Leicester da alaka da ta'addnci. Da maraicen Lahadi ne dai fashewar ta auku a kan titin birnin da ke cike da gidaje gami da zirga-zirgar jama'a. Lamarin ya tilasta yanke wutar lantarki a gidaje da dama saboda bai wa jami'an agaji damar kai dauki.
Jami'an 'yan sanda da na kwana-kwana, sun ja hankalin kafofin watsa labarai da su guji karin gishiri kan lamarin, musamman ma alakanta shi da ta'addancin. Jami'an sun kuma ce suna ci gaba da gudanar da bincike, kuma nan gaba kadan za su sanar da cikakken abin da ya auku.