Hare haren ƙunar baƙi wake a Irak
February 3, 2013Talla
An ba da rahoton cewar mutane a ƙalla guda 33 ne suka kwanta dama a harin wanda aka kai a garin Kirkuk da ke a yankin arewacin ƙasar Irak yayin da wasu guda 90 suka jikata.
Shaidu sun ce wani ɗan ƙunar baƙin wake ne, ya tayar da bam a sa'ilin da mutane ke fita zuwa wurin inda bam ɗin ta rusa wani ɓangare na wani ginin gwamnati. Majiyoyin likitoci sun ce daga cikin waɗanda suka mutu 12 ma'aikata ne a ginin ofishin gwamnatin da ya faɗi. Shi ma dai wanda ya kai harin da ke tare da rakiyar wasu maharan guda biyu ya mutu a cikin harin.Yazuwa yanzu babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin kai harin.
Mawallafi : Abdourahamne Hassane
Edita : Halima Balaraba Abbas