1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hare-hare a Afganistan

September 17, 2010

Ƙungiyar Taliban ta yi awan gaba da wasu mutane a jajibirin zaɓen ´yan majalisa

https://p.dw.com/p/PEmy
Ƙungiyar Taliban ta kai hare-hare a AfganistanHoto: AP

   Ƙungiyar mayaƙan taliban a ƙasar Afganistan ta yi awan gaba da wasu mutane guda 19 a ciki hadda ɗan takara guda, a jajibirin zaɓen ´yan majalisun da za a gudanar a ƙasar a gobe asabar idan Allah ya kaimu

Mutanen waɗanda suka haɗa da ´yan siyasa da kuma wasu ma´aikatan hukumar zaɓen  an sace su ne a Bad-ghis yankin da ke a arewa maso yammacin ƙasar

Kimanin mutane miliyan goma ne ake sa ran zasu kaɗa ƙuri´a a zaɓen domin zaɓen wakilan ´yan majalisun na jirga 249

Sai dai a halin da ake ciki masu lura da al'amuran yau da gobe na hasashen cewa jama´a ƙalilan ne zasu fito saboda barazanar da ƙungiyar ´yan taliban ɗin ta yi na kai hare hare a runfunan zaɓen

Mawallafi: Abdourahman Hassane

Edita: Yahouza Sadissou Madobi