1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hamas da Fatah sun cimma yarjejeniya kan Gaza

Mohammad Nasiru AwalSeptember 25, 2014

Kungiyoyin Fatah da Hamas sun amince su mika ikon Gaza ga gwamnatin hadaka ta Faladinu.

https://p.dw.com/p/1DLDb
Gaza Verhandlungen Einheitsregierung Fatah Al-Ahmad Hamas Musa Abu Marzouk
Hoto: Khaled Desouki/AFP/Getty Images

Kungiyoyin Falasdinawa da ba sa ga maciji da juna wato Hamas da Fatah sun cimma wata yarjejeniya a wannan Alhamis, inda gwamnatin hadin kan kasa karkashin jagorancin Shugaba Mahmud Abbas za ta karbi iko da Zirin Gaza. Masu shiga tsakani a tattaunawar da bangarorin ke yi a birnin Alkahira na kasar Masar suka sanar da cimma wannan yarjejeniya. Azzam Ahmed na kungiyar Fatah ya ce dukkan ma'aikatan gwamnati za su rika samun albashi daga gwamnatin hadin kai domin dukkansu Falasdinawa ne kuma gwamnati ce ta dukkan Falasdinawa.