1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hadin kan aikin raya kasa da kasashe masu fama da rikici

July 11, 2013

Huldar aikin raya kasa da kasashe masu fuskantar barazanar rugujewa kamar Mali na tattare da matsaloli ga masu ba da taimakon kamar tarayyar Jamus.

https://p.dw.com/p/19656
Mali's interim President Dioncounda Traore (L) shakes hands with Germany's Minister of Economic Cooperation and Development Dirk Niebel (R) during their meeting in Bamako on March 23, 2013. Niebel called for Mali's authorities to hold as planned elections in July, a condition for the full recovery of German help in the African country in crisis for a year. AFP PHOTO / HABIBOU KOUYATE (Photo credit should read HABIBOU KOUYATE/AFP/Getty Images)
Hoto: Habibou Kouyate/AFP/Getty Images

Kasar Mali ta dauki lokaci mai tsawo tana zaman kyakyawar abar misali a tsakanin kasashen Afirka. Amma cikin lokaci kankane ta koma jerin kasashe masu fuskantar barazanar rugujewa. Tarayyar Jamus dake ba da taimakon raya kasa na fama da matsalolin yin hulda da irin wadannan kasashe kamar Mali dake yankin yammacin Afirka.

Yakin da aka shafe shekara daya da rabi ana yi a arewacin Mali da kuma dambarwar siyasa a Bamako babban birnin kasar sun bar babban tabo a kasar, inda aka tilasta wa dubbban daruruwan mutane barin yankunansu na asali. Tun gabanin yakin kasar ma Bankin Duniya ya nuna cewa fiye da rabin al'ummar kasar ta Mali na fama da matsanancin talauci da rashin ilimi da karancin tsabtataccen ruwan sha da kuma yawan mace-macen yara.

Mabanbantan matsaloli a kasashen da babu tabbas

Elderly women rest as Malian refugees from the north arrive at the new UNHCR Imbaidou refugee camp, on May 29, 2012, near Ayorou, north-west of Niamey in Niger, where Malian refugees have found shelter. African Union chief Thomas Boni Yayi called on May 30 for the creation of a UN-backed force to intervene in Mali, where Islamist militants and Tuareg rebels have declared independence in the north. AFP PHOTO / ISSOUF SANOGO (Photo credit should read ISSOUF SANOGO/AFP/GettyImages)
Rikicin Mali ya tilasta wa dubban 'yan kasar barin yankunansuHoto: Issouf Sanogo/AFP/GettyImages

Mali da kasashe kamar Somaliya, Cotre d'Ivoire da kuma Afghanistan na a jerin kasashe masu fuskantar barazanar rugujewa ko da yake matsalolinsu sun bambamta. Wibke Hansen ita ce mataimakiyar daraktan cibiyar nazarin ayyukan samar da zaman lafiya ta kasa da kasa dake birnin Berlin, ta yi karin haske a kan wanna batu tana mai cewa:

"Kasashe masu rauni ko suke da dab da rugujewa kasashe ne da ba sa iya tsaron yankunansu na cikin gida da kan iyakokinsu. Ba sa kuma iya tabbatar da ikon gwamnati da tsaron lafiya jama'arsu. Ba sa kuma da karfin samar da isasssun ababan more rayuwa kamar ilimi da kiwon lafiya ga al'umma."

Sama da rabin kasashen dake hulda da Jamus a bangaren hadin kan ayyukan raya kasa na a jerin kasashe dake fuskantar barazanar rugujewa ko kuma ke fama da rikice-rikice. Baya ga hadin kan ayyukan raya kasa wani muhimmin batu shi ne na tsaro, domin kasashen da ba sa iya tabbatar da tsaron kan iyakokinsu ko wasu yankuna na cikin gida, suna iya zama wata matattarar 'yan ta'adda.

Burkinabe soldiers, part of the MISMA African forces in Mali, receive blue berets to signify the change of mission command to the UN in Timbuktu June 30, 2013. The 12,000-strong U.N. peacekeeping mission in Mali, MINUSMA, is due to start on July 1. REUTERS/Adama Diarra (MALI - Tags: POLITICS MILITARY)
Sojojin duniya na taka rawa wajen maido da zaman lafiya a MaliHoto: Reuters

Muhimmancin inganta lamirin tsaro

A bara ma'aikatar harkokin wajen Jamus da ta tsaro da kuma ta raya kasashe masu tasowa sun fitar da wani tsari dake nuni da yadda gwamnatin tarayyar Jamus za ta yi hulda da kasashe masu fama da rikice-rikice. Dirk Niebel shi ne ministan dake kula da hadin kan ayyukan raya kasashe masu tasowa na Jamus, da ya ce:

"Ba na jin gwamnatin Jamus za ta yarda wata kasa kamar Mali ta fada hannun kungiyoyin 'yan ta'adda. Yanzu haka baya ga sake gina kasar, muna kuma taimakawa wajen fadada tsare-tsarenta na tsaron kasa."

Sannu a hankali dai Jamus ta farfado da aikin taimakon raya kasa ga Mali bayan dakatar da shi a farkon shekarar 2012 biyo bayan juyin mulkin soji da sojoji suka yi a kasar. Burin aikin da Jamus din ke yi a Mali dai ya hada da sake daidaita al'amura a kasar wadda ke shirin gudanar da zabukan gama gari a ranar 28 ga watan Yuli.

Mawallafa: Sven Pöhle / Mohammad Nasiru Awal
Edita: Saleh Umar Saleh