Iyalan Gupta da siyasar Afirka ta Kudu
February 15, 2019Talla
Babu dai cikakkun bayanai kan dalilan soke sammacin kama fitaccen dan kasuwar da ake zargi da cin hanci da rashawa, amma hukumar 'yan sandan ta ce za ta iya sabunta sammacin. Lauyan da ke kare Gupta da iyalansa a kotun dai bai yi martani kan matakin hukumar 'yan sandan ba.
An dai jima ana zargin iyalan Gupta da laifukan cin hanci da neman yin sama da fadi da dukiyar kasar ta Afirka ta Kudu ta hanyar amfani da ikon tsohon shugaban kasar Jacob Zuma da ake cewa akwai alaka ta abota a tsakaninsu, sai dai Gupta ya sha karyata duk wani zargi na rashawa tare da nesanta kansa da duk wata dangantaka da Zuma.