1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gangamin adawa da tazarce a Kwango

Yusuf BalaAugust 23, 2016

A ranar Talatan nan dai a kwai karancin jama'a a titunan birnin Kinsasha saboda kiran shiga yajin aikin na gama gari da 'yan adawa suka kira a fadin kasar.

https://p.dw.com/p/1Jniu
Kongo Demonstration der Opposition in Kinshasa
'Yan adawa dai na kokari na ganin Shugaba Joseph Kabila bai yi tazarce baHoto: Getty Images/AFP/E. Soteras

'Yan adawa da shugaban kasar Kwango sun gudanar da wani gangami a ranar Talatan nan bayan da suka kira wani yajin aiki na gama gari bisa bukatarsu ta ganin shugaban kasar ya sauka daga mukaminsa da zarar ya kammala wa'adin mulkinsa a watan Disamba mai zuwa.

'Yan sanda dai sun yi amafani da hayaki mai sa hawaye wajen tarwatsa gangamin daruruwan mutane a shedikwatar 'yan adawa mafi girma da ke lardin Limete a Kinsasha kamar yadda wadanda suka ga lamarin suka sheda wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Da safiyar Talatan nan dai a kwai karancin jama'a a titunan birnin Kinsasha sabanin yadda aka saba, wasu shaguna a rufe, wasu mutane na zaune a gidajensu. Sai dai a bangaren kamfanoni na hakar ma'aidanai da anan ne 'yan kasashen waje suka fi zuba jari harkoki na gudana. a