1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gabon: Alain-Claude Bilie-By-Nze ya zama sabon firaminista

Abdoulaye Mamane Amadou
January 9, 2023

Kwanaki bayan da jam'iyyar da ke mulki ta bukaci ya zarce kan karagar mulki, shugaba Ali Bongo Ondimba na kasar Gabon ya aiwatar da sabbin sauye-sauye a harkokin mulki

https://p.dw.com/p/4Lvaj
Sabon firaministan Gabon  Alain-Claude Bilie By Nze
Sabon firaministan Gabon Alain-Claude Bilie By NzeHoto: STEEVE JORDAN/AFP

Shugaba Ali Bongo Ondimba na kasar Gabio ya nada  Alain-Claude Bilie-By-Nze a matsayin sabon firaministan kasar a wannan Litini, inda zai maye gurbin  Rose Christiane Ossouka Raponda, da za ta kasance mataimakiyar shugaban kasa.

Fadar shugaban kasar ce ta sanar da haka, a daidai lokacin da masu adawa da gwamnatin Ali Bongo ke cigaba da korafi kan rashin iya mulki.

Bilie-By-Nze, mai shekaru 55 a duniya, ya taba rike manyan mukamai a cikin gwamnatin Bongo Ondimba tun a shekarar 2006, ciki har da ministan makamashi da mukamin mataimakin firaminista