1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Kasashen G7 za su kara taimaka wa Ukraine

Abdoulaye Mamane Amadou LMJ
May 13, 2022

A yayin taron kolin ministocin harkokinsu na waje, kasashen G7 mafi karfin arzikin masana'antu, sun bayyana anniyarsu ta kara tallafa wa Ukraine a yakin da take da kasar Rasha.

https://p.dw.com/p/4BGh1
Deutschland | G7 Außenministertreffen | Annalena Baerbock
Hoto: Felix Zahn/photothek/IMAGO

Birtaniya ta bayyana cewa dole ne a dafa wa Ukraine da karin manyan makamai na yaki, haka da kakaba wasu karin takunkumai kan Rasha, a yayin da ita kuwa Faransa ta bayyana goyon bayan kungiyar NATO face sai Ukraine ta yi nasara a yakin da take da Rasha.

Kungiyar Tarayyar Turai ta da dauki alkawarin bada karin kudade Euro miliyan 500 ga Ukraine. Sai dai da yake mayar da martani a yayin wata ziyarar da ya kai a Tadjikistan, ministan harkokin wajen Rasha Sergueï Lavrov ya zargi tarayyar Turai da kai ruwa rana a rikicin da kasar ta ke da Ukraine.

Rashar dai na cigaba da yi wa Ukraine barin wuta ta sama da kasa, inda ko a wannan Jumma'ar ma'aikatar tsaron kasar ta ce ta kai wasu jerin hare-hare da maiamai masu linzami kan wata matatar mai a yankin Poltava da ke gabashin Ukraine din tare da lalata dumbin runbun tsimi na man fetur.