Habasa ta yi ikirarin nasara
January 19, 2021Talla
Shugaba Abiy Ahmed na kasar Habasha ya ayyana nasara ga dakarun gwamnati a yakin basasar da kasar ta gwabza watanni biyu da suka gabata.
Sai dai wasu alamu na nuni da cewa akwai sauran rina a kaba, bisa la'akari da sakwannin barazana da dakarun na Tigray ke aikewa dasu a 'yan kwanakin nan.
A karshen watan Nuwamban bara ne dakarun gwamnati suka karbe Makele, birni mafi girma da masu boren ke tinkaho da shi, wanda ya tilastawa dubban mazauna yankin yin gudun hijira.