1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fargaban ƙasashen duniya a kan Libiya

Abdourahamane HassaneJanuary 27, 2016

Manzon musammun na MDD a Libiya Martin Koblers ya bayyana rashin gajen dangana na ƙassahen duniya a kan gazawa na 'yan siyasa na Libiya na aiwatar da shirin zaman lafiya.

https://p.dw.com/p/1HkvN
Martin Koblers Besuch in Libyen
Martin Koblers Manzon musammun na MDDHoto: picture alliance / dpa

Hakan kuwa na zuwa ne kwanaki biyu bayan da majalisar Tobruk ta yi watsi da shirin gwamnatin haɗin kan ƙasa a Libiyar wanda aka cimma a makon jiya.Koblers wanda ke yin magana da 'yan jaridu a birnin Tunis ya ce ƙungiyar IS na ƙara danawa a yankin kudancin Sahara.


Abin da ke zaman barazana ta ƙara bazuwar aiyyukan ta'addanci a ƙasashen Chadi da Nijar sannan kuma ya ce a gobe za su gudanar da taron kan batun tare da Ƙungiyar Tarrayar Afirka a Habasha.