Fafutukar cimma maradun ƙarni a Najeriya.
April 25, 2013Manyan abubuwan da ake mayar da hankali akan su na maradun ƙarni guda takwas sune : rage yawan talauci, da inganta sha'anin illimi, da kiwon lafiya, da sha'anin noma da kiwo , da yaƙi da ciwon SIDA, da rage yawan mutuwar yara ƙanana, kana kuma da samar da yanayin gewayen ɗan adam mai kyau,da dai sauran su.
Ƙasashen duniya manbobin Majalisar Ɗinkin Duniya guda 193 da wasu ƙungiyoyin masu fafutuka 23 suka haɗu suka rataɓa hannu akan wannan yarjejeniya a birnin New York, na Amurika a shekarun 2000.
To amma misali Tarrayar Najeriya da ke ɗaya daga cikin ƙasashen da suka amince da shirin har yanzu rayuwar al'umma na daɗa yin muni. Ga yuwan ga talauci, sannan babu issasun magunguna a asibitoci, kuma filayen da ake noma wa na ƙara ja da baya. Shin ko za a iya cimma wannan ɓuri kafin shekarun na 2015, wannan ita ce tambayar da na yi wa Adamu Mohammed wani jami'in da ke kula da shirin a Jigawa.
Ya ce: ''Ƙasashe kamar namu ko da an cimma shirin ɗari bisa ɗari, ba zai yiwu ba a kwatantasu da ƙasashen da suka ci- gaba.''
Najeriya dai mai yawan al'umma sama da miliyan ɗari , jama'a da dama ne ke yin rayuwa da ƙasa da dalla Amurika ɗaya a yini, abinda ke zaman koma baya ga ci gaban tattalin arzikin ƙasar da kuma na jin dadin rayuwar al'ummar. Jahar Jigawa dai na ɗaya daga cikin jihohin Tarrayar Najeriya da ake ƙaddamar da shirin na MDG
Mawallafiya : Zainab Shuaib Rabo
Edita : Abdourahamane Hassane