1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU za ta yi taro kan rikicin Ukraine

Ahmed SalisuJanuary 25, 2015

Kungiyar tarayyar Turai ta kira taro na gaggawa na ministocin harkokin wajen kasashen da ke cikin kungiyar don tattaunawa kan sabon rikicin da ya barke a gabashin Ukraine.

https://p.dw.com/p/1EQJ5
Flagge der EU
Hoto: picture alliance/Wolfram Steinberg

Kantomar da ke kula da harkokin kasashen ketare ta kungiyar ta EU Federica Mogherini ta ce a wannan Alhamis din da ke tafe ce za a gudanar da wannan taro da nufin samo hanyoyin warware wannan sabon tashin hankalin.

A 'yan kwanakin da suka gabata gabashin Ukraine din ya fuskanci rikici da ya yi sanadin rasuwar mutane da dama musamman ma a Mariupol a ranar Asabar bayan wani hari da aka kai na rokoki.