1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU ta kakaba wa Belarus takunkumi

May 25, 2021

Kungiyar tsaro ta NATO ta bakin babban sakatarenta Jens Stoltenberg ta yi marhabin da matakin da kasashen Kungiyar Tarayyar Turai suka dauka na kakaba wa Belarus takunkumin dakatar da sufurin jiragen sama a kasar.

https://p.dw.com/p/3tvRN
Belarus | Symbolbild Beziehungen EU und Belarus
Hoto: Leonid Faeberg/Russian Look/picture alliance

Matakin na EU na zuwa ne a wannan Talatar sakamakon abin da mahukuntan birnin Minsk suka yi ranar Lahadin da ta gabata na tursasawa wani jirgin fasinjoji yin saukar gaggawa a kasar tare da kame wani dan adawa da ke kan hanyarsa ta yin bulaguro.

Shuwagabannin kasashen kungiyar sun yi tir da wannan matakin na mahukuntan Belarus din duk kuwa da uzurin da suka bayar na cewa sun tilasta wa jirgin saukar gaggawar ne sanadiyar rahotannin da suka samu na cewa akwai wani abu mai fashewa a cikin jirgin.