1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU ta ce ficewar Birtaniya na nan

May 24, 2019

Tarayyar Turai ta ce matsayinta kan batun ficewar Birtaniyar daga gamayyar kasashen Tura na nan da fashi kamar yadda kasar ta sanya hannu.

https://p.dw.com/p/3J1ra
Theresa May London Statement
Hoto: Reuters/T. Melville

Kungiyar Tarayyar Turai ta EU, ta ce murabus din Firaministar Birtaniya ba zai sauya matsayinta a kan batun ficewar Birtaniyar daga gamayyar kasashen Turan, kamar yadda kasar ta sanya hannu ba.

Shugaban EUn Jean-Claude Juncker ya ce majalisar Turan ta kammala daukar matsaya dangane da bukatar Birtaniyar, lokaci ne kawai ake jira.

A yau ne dai Firaministar Birtaniya Theresa May, ta bayyana cewa za ta ajiye aiki a ranar bakwai ga watan gobe na Yuni.

"A yau ina sanar da cewa ranar 7 ga watan Yuni zan yi murabus daga shugabancin jam'iyyar Conservative da na yi farin cikin rikewa, hakan zai ba da damar zaben sabon firaiminista. Lallai ina ajiye aiki mai daraja a rayuwata. Ni ice firai Minista mace ta biyu, amma tabbas ba ta karshe ba"  

Theresa May ta fuskanci matsi daga 'yan kasar a kan shirin ficewa daga kungiyar da aka sani da Brexit.

Sau uku kudurinta ya gaza nasara a majalisar Birtaniyar dangane da ficewar kasar.