1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU ta ƙuduri aniyar bada horo ga sojojin Mali

January 28, 2013

Dakaru fiye da 400 na ƙungiyar Tarayyar Turai za su koyar da sojojin Mali dubarun yaƙi da ta'adanci, da ɗabi'o'in aikin soja.

https://p.dw.com/p/17Slv
©Ange Obafemi/PANAPRESS/MAXPPP - 17/01/2013 ; ; Togo - LOME - JANUARY 17: A hundred of Togolese soldiers leave the international airport to Mali on January, 17 2013 in Lome, Togo. Some 500 Togolese soldiers are required to join the international force in Mali. (Photo Ange Obafemi /Panapress) - LOME - 17 JANVIER: Une centaine de soldats togolais quittent l'aeroport international pour le Mali. Lome, Togo, 17 janvier 2013. Le Togo doit envoyer quelques 500 soldats au Mali. (Photo Ange Obafemi /Panapress)
Hoto: picture-alliance/dpa

Ranar 17 ga watan da mu ke ciki ne ƙungiyar Tarayya Turai, ta yanke hukunci tura dakaru a Mali ,domin bada horo ga sojojin ƙasar ta yadda za su iya fuskantar ƙalubalen 'yan ta'ada da ke baraza ga ƙasar.

Sojoji 400 zuwa 450 ne ƙungiyar tarayya Turai za ta turawa a ƙasar Mali, saidai saɓanin dakarun Faransa da ke fafatawa a fagen yaƙi, sojojin na EU za su zama a birnin Bamako domin bada horo ga takwarorinsu na Mali.Babban burin da ake buƙatar cimma shine: sojojin Mali su laƙanci husa'o'in yaƙi domin zuwa gaba su cece ƙasarsu da kansu, domin a cewar Richard Zink shugabar tawagar ƙungiyar tarayya Turai a ƙasar Mali koyar da mutum kamin kifi ya fi ka ba shi kifi a gashe:

Ya ce:Cemma EU ta saba shirya makammacin wannan horo a Afrika.Irin sa ne sojojin Somaliya su ka samu.Kuma a tsukin shekaru biyu, dakarun Somaliya suka laƙanci dubarun gwagwarmaya tare da 'yan ta'ada.

Sakamakon da aka cimma a Somaliya ya nunar da cewa kwaliya ta biya kuɗin sabulu.

A U.S. Special Forces Green Berets, right, inspects the weapons of Malian soldiers from the 512th Motorised Infantry company during an ambush training exercise in the desert near Timbuktu, Mali Wednesday, March 17, 2004. The training is part of the U.S. Pan-Sahel Initiative which aims to help soldiers in Mali, Niger, Chad and Mauritania boost battle skills amid the worldwide fight against terrorism. (AP Photo/Ben Curtis)

Saidai al'amarin ƙasar Mali ya na da sarƙaƙiyya inji Professa Modibo Goita domin a shekarun baya , kasar Amirka ta hiora da sojojin Mali dubarun yaƙi da aiyukan ta'adanci, amma a ka wayi gari sojojin da suka samu horan su ka cenza sheƙa zuwa rundunonin tawaye da na ƙungiyoyin ta'adanci:

"Sojojin da Amurika ta ba horo sun tsere da motoci kira Toyota masu shiga yashi fiye ta 80.Akasarin wanda suka samu horon sun fito daga yankin arewancin ƙasa.

Gwamnati ta amince da hakan, domin kaucewa zargin nuna bambancin launin fata a cikin rundunar soja, da zumar cimma burin haɗin kan ƙasa."

Sojojin da suka samu horo daga Amirka, sun kasance daga shika-shikan da su ka girka ƙungiyar tawayen MNLA mai fafutakar samun 'yancin kan yankin Azawad.

A yanzu babban ƙalubalen da ke gaban tawagar sojojin EU a ƙasar Mali shine faɗakar da dakarun ƙasar game da da mahimmancin haɗin kan ƙasa, biyyaya da kuma sadaukar da kai, abubuwan da ke samun ƙarancinsa a ƙasar Mali inji Panya Harivongs wani soja na ƙasar Faransa da ya jima ya na aiki a Mali,ya ce:

A ƙasashe da dama na Afirka ana shiga aikin soja ne ba dan wai ana shawar aikin ba, a'a saboda da dai kawai a samu wurin cin abinci.

Malian soldiers wait at a checkpoint near Sevare on January 27, 2013. French-led troops were advancing on Mali's fabled desert city of Timbuktu on Sunday after capturing a string of other towns in their offensive against Islamist militant groups in the north of the country. Meanwhile, African leaders meeting in the Ethiopian capital were discussing scaling up the number of African troops to join the offensive, after the African Union's outgoing chief admitted the body had not done enough to help Mali. AFP PHOTO / FRED DUFOUR (Photo credit should read FRED DUFOUR/AFP/Getty Images)
Hoto: Fred Dufour/AFP/Getty Images

A ƙasar Mali matsalar ta fi tsanani domin babu biyyaya ga girmamawa tsakanin sojojin.Sannan a mafiya yawan ƙasashen Afirka su kansu shugabanin ƙasashe su na da babban lefi a cikin taɓaɓarewar al'amura a rundunar sojoji, domin sun fi daba fifiko ga sojojin dake tsaron lafiyarsu fiye da sojojin da ke tsaron ƙasa.

Ta la'akari da halin da ƙasar Mali ta shiga a yanzu, ƙila ya zama darasi da shugabanin ƙasar da ma na Afirka game da mahimmancin samar da rundunar soja ƙwaƙƙwara wadda za ta kula da tsaron ƙasa.

Mawallafa: Gänsler Katrin da Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani